in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Al'ummar Zambiya na ban kwana da marigayi shugaba Sata
2014-11-12 16:31:44 cri
Dubun dubatar al'ummar kasar Zambiya sun yi dandazo a birnin Lusaka, domin halartar bikin binne gawar shugaban kasar Michael Sata, wanda ya rasu cikin watan da ya gabata.

Iyalai da abokan arzikin marigayin sun shiga jerin wakilan gwamnati, tare da baki daga kasashen waje, domin gudanar da addu'o'i na musaman ga shugaba Sata, taron da ya gudana ne a jiya Talata.

Yayin taron na jiya shugaban rikon kwaryar kasar ta Zambiya Guy Scott, ya bayyana cewa aikin da ya sanya gaba shi ne, tabbatar da nasarar zaben shugabancin kasar cikin nasara.

Marigayi shugaba Sata dai ya rasu ne yana da shekaru 77 a duniya, a wani asibiti dake birnin Landan. A yanzu haka kuma gwamnatin kasar ta ware makwanni 2, domin baiwa al'ummar kasar damar zaman makokin shugaban kasar.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China