in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar Internet.org ta fara samar da ayyukan hidima ga nahiyar Afirka ba tare da karbar ko kwabo ba
2014-08-26 15:19:28 cri
Kungiyar Internet.org wadda ta kasance wata kungiyar kasa da kasa mai samar da ayyukan hidima a fannin yanar gizo ko Intanet, ta fitar da wata sabuwar manhaja bisa tsarin Android a kasar Zambia a kwanakin baya, wadda ke iya baiwa mazauna wurin damar amfani da Intanet ba tare da biyan ko kwabo ba.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, ta hanyar amfani da wannan manhaja, jama'ar kasar Zambia za su iya shiga shafukan Intanet na Facebook, da Google, da WikiLeaks da dai sauransu, kana za su iya samun labarai a fannonin kiwon lafiya, da na guraban ayyukan yi, da hasashen yanayi, da kuma na kare hakkin mata kyauta. Sai dai kasancewar Internet.org din na hadin gwiwa ne da kamfanin sadarwa na Airtel na kasar Zambia shi kadai, ya sa masu shiga tsarin Airtel a kasar Zambia kawai ne za su iya samun wannan hidima. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China