in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tsohon shugaban kasar Zambiya na shirin dawowa fagen siyasa
2014-10-07 15:51:57 cri
Tsohon shugban kasar Zambiya Rupiah Banda ya bayyana cewa a shirye yake na dawowa fagen siyasa idan har jam'iyyarsa na fatan ganin halartarsa a zabubukan kasar na shekarar 2016, in ji wata jaridar Zambia Daily Mail a ranar Litinin.

Yanzu akwai kiraye-kiraye da dama dake fitowa daga cikin jam'iyyar MMD dake bukatar tsohon shugaban kasar ya dawo fagen siyasa da fatan ganin halartarsa a zabubukan shekarar 2016 a matsayin dan takarar jam'iyyar.

Wasu bangarorin da suka balle daga tsofuwar jam'iyyar mai mulki, da ta fadi a zabubukan shekarar 2011 bayan shekararu ashirin tana mulkin kasar Zambiya, sun zargi shugaban jam'iyyar na yanzu Nevers Mumba da kasancewa mugun shugaba kuma wanda ya kashe jam'iyyar bayan jerin rashin nasarorin da ta samu a zabubukan 'yan majalisa.

Tsohon shugaban Zambiya ya shaida wa 'yan jarida a birnin Chipata inda aka haife shi dake gabashin kasar Zambiya cewa a shirye yake na dawowa fagen siyasa idan 'yan kasar Zambiya na bukatar haka din.

Ya bayyana cewa zaben dan takarar jam'iyya da zai tsaya a zaben shugaban kasa na shekarar 2016 ba zai yiwu ba sai idan an samu yin shawarwari tare da shugaban jam'iyyar na yanzu.

Mista Banda, mai shekaru 77 da haifuwa, ya janye daga fagen siyasa bayan da ya fadi a zaben shekarar 2011. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China