A ranar Larabar nan ne majalisar ministocin kasar Zambia ta sanar da rasuwar shugaban kasar Michael Sata, bayan ya sha fama da wata jiyya.
Da ma dai batun yanayin lafiyar shugaba Sata ya dade yana janyo hankalin kasa da kasa, duba da cewa watanni uku ke nan ba a ga fuskarsa a bainal jama'a ba.
A baya akwai rahotannin da ke cewa, ya ziyarci kasar Isra'ila domin neman magani, ko da yake gwamnatin kasar ta musanta hakan, tana mai cewa, hutu shugaban ya tafi. (Zainab)