in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban hafsan Burkina Faso ya sanar da rusa gwamnati da majalisar dokokin kasar
2014-10-31 11:06:08 cri
Bisa labarin da aka samu, an ce, jiya Alhamis 30 ga wata, hafsan hafsoshin rundunar sojan kasa ta Burkina Faso Honore Nabere Traore ya sanar a babban birnin kasar, Ouagadougou cewa, an dakatar da tsarin mulkin kasa da kuma rusa gwamnati da majalisar dokokin kasar.

Sanarwar ta nuna cewa, an tsai da kudurin sakamakon samun tashe tashen hankali da zanga-zangar masu adawa da gwamnatin a duk fadin kasar.

Haka kuma, sanarwar ta bayyana cewa, domin magance ci gaban tabarbarewar yanayin siyasa a kasar, shugaba Blaise Compaore da firaminista Luc-Adolphe Tiao sun cimma ra'ayi daya cewa, za a gudanar da babban zaben kasar cikin watanni 12 masu zuwa, kana ana kira ga jama'ar kasa da su dukufa wajen kai zuciya nesa a lokacin sauyin yanayin siyasa, don magance haddasa karin barazana ga yanayin kasar.

A wannan rana, an gudanar da babbar zanga-zanga a kasar Burkina Faso sakamakon yunkurin shugaban kasar yayi na kawo gyaren fuska ga kundin tsarin mulkin kasar don neman yin tazarce. Kuma bisa labarin da jam'iyyar adawa ta kasar ta bayar, an ce, zanga-zanga ta riga ta haddasa rasuwar mutane 30, yayin da wasu fiye da dari suka jikkata.

Dangane da lamarin, babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya ba da wata sanarwa ta bakin kakakinsa cewa, yana damuwa sosai don gane da yanayin da kasar Burkina Faso take ciki a halin yanzu, ya kuma yi kira da a dakatar da tashe tashen hankali, da kuma warware dukkanin matsalolin kasar ta hanyar yin shawarwari. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China