in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwadebuwa da Burkina Faso za su karfafa hadin gwiwar da ke tsakaninsu
2013-07-31 10:56:25 cri
A ranar 30 ga watan nan ne aka kira taron shugabannin kasashen Kwadebuwa da Burkina Faso karo na uku, a birnin Yamoussoukro na kasar Kwadebuwa, bisa yarjejeniyar abokantaka da hadin gwiwa da aka kulla tsakanin kasashen biyu.

Yayin taron bangarorin biyu sun nuna fatan kara wasu kudurori cikin yarjejeniyar tasu, domin zurfafa hadin gwiwar da ke tsakaninsu, tare da sa hannu kan karin yarjejeniyoyin hadin gwiwa guda 19. A jawabinsa ga mahalarta taron, shugaban kasar Kwadebuwa Alassane Ouattara ya bayyana amincewarsa da sabbin manufofin ci gaba da hadin gwiwa da aka kara cikin yarjejeniyar abokantaka da hadin gwiwa wadda kasashen biyu suka kulla a shekarar 2008. Ya kuma yi imanin cewa dangantaka da hadin gwiwar da ke tsakanin kasashen biyu za su ci gaba da bunkasa ya zuwa wani sabon matsayi.

Shi ma a nasa tsokaci, shugaban kasar Burkina Faso Blaise Compaore cewa ya yi, an sa hannu kan sabbin yarjejeniyoyin ne don karfafa hadin gwiwa da cinikayyar da ke tsakanin kasashen biyu, da kuma gina hanyoyin mota na zamani, da layin dogo domin jiragen kasa, da kuma raya ayyukan noma da sufuri. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China