in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Sin ya gana da Ban Ki-moon
2014-09-26 20:30:35 cri
Jiya Alhamis 25 ga wata, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya halarci liyafar cin abincin rana da babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya shirya wa ministocin zaunannun mambobi kasashen kwamitin tsaron MDD da suka halarci babban taron MDD

A yayin liyafar, ministocin kasashe biyar sun yi musayar ra'ayi da Ban Ki-moon kan batutuwan da suka shafi yaki da ta'addanci, yanayin yankin Gabas ta Tsakiya, yaki da cutar Ebola da sauran batutuwan dake janyo hankulansu matuka, inda suka cimma matsayi daya cewa, a halin yanzu, ana fama da matsaloli a wasu yankunan kasa da kasa, wadanda suka haifar da illa ga zaman lafiya da tsaron kasa da kasa. Kuma ya kamata zaunannun mambobi kasashen kwamitin tsaron MDD su dauki mataki na musamman don warware matsalolin, bugu da kari, ya kamata kasa da kasa su yi hadin gwiwa kan wannan batu da kuma goyi bayan aikin da babban magatakardan Ban Ki-moon yake yi kan wadannan batutuwa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China