in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Uganda ya fara jagorantar babban taron MDD karo na 69
2014-06-12 14:44:21 cri
An zabi ministan harkokin wajen kasar Uganda Sam Kutesa, a matsayin shugaban babban taron MDD karo na 69 a jiya Laraba 11 ga watan nan, yayin cikakken zaman taron majalissar karo na 68.

Shugaban babban taron MDD karo na 68 John Ashe ne ya sanar da sakamakon zaben, tare da taya Mr. Kutesa murnar zaben nasa.

Tuni dai Kutesa ya bayyana shirin aikinsa a matakin farko, inda ya bayyana cewa, zai ci gaba da inganta manufar ci gaba bayan shekarar 2015, tare da sanya "shirin gudanar da manufofin neman ci gaba bayan shekarar 2015" a matsayin taken babban taron MDDr a karo na 69.

A nasa bangare babban magatakardan MDD Ban Ki-moon, wanda ya halarci taron na ranar Laraba, ya yi wa Mr. Kutesa fatan alheri, tare da bayyana shi a matsayin gogagge a fannoni daban daban. Har ila yau Mr. Ban ya yi fatan babban taron MDDr zai samu nasara mai gamsarwa, game da cimma burin kawar da talauci na shekarar 2000, da kuma kudurorin neman ci gaba bayan shekarar 2015, a karkashin jagorancin Mr. Kutesa.

Bugu da kari, Mr. Ban ya jaddada cewa, taron koli game da sauyin yanayi da za a kira a watan Satumba a hedkwatar MDD, zai kasance babbar dama ta neman cimma nasarar shawarwari game da batun na sauyin yanayi. Ya kuma ce za a gudanar da taron koli a yayin taron da za a yi daga watan Satumba zuwa na Disamba a yayin babban taron MDDr karo na 69. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China