in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci Libya da ta warware matsalolinta bisa karfin kanta
2014-09-18 14:47:40 cri
Wakilin musamman na MDD, Bernardino Leon, ya bayyana a ranar 17 ga wata a birnin Madrid cewa, MDD za ta yi kokarin taimakawa Libya wajen warware rikicinta na cikin gida. Amma ya nuna cewa, ya kamata kasar Libya ta warware matsalolinta da kanta. Ya bukaci shugabannin kasar da su mai da hankali kan hakikanin yanayin da ake ciki a kasar da daukar matakai cikin sauri, da kuma yin shawarwari karkashin wata halaltacciyar gwamnatin da aka zaba.

Wakilai daga kasashe, yankuna da kungiyoyin duniya kusan 21 suka halarci wani taron kasa da kasa game da batun tabbatar da zaman lafiya da bunkasuwa a kasar Libya a ranar 17 ga wata a birnin Madrid, inda firaminstan kasar Sifaniya Gobierno Rajoy ya yi kira da a kafa wata kasar Libya mai ikon kanta, inda ake samun hadin kan al'umma, da wadata, gami da tsarin demokuradiyya.

A nasa bangaren, ministan harkokin wajen kasar Libya Mohamed Abdel-Aziz ya bayyana cewa, kasarsa ta Libya ba ta da cikakken karfi wajen tinkarar kalubalen da take fuskanta, don haka tilas ne gamayyar kasa da kasa ta taimaka wajen yaki da kungiyoyin ta'addanci da kuma yanke hukunci kansu. Kana kamata ya yi kasa da kasa su dauki matakai don hana 'yan ta'adda na wasu kasashe shiga kasar Libya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China