in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na M.D.D. ya tsawaita wa'adin ofishinsa wajen tabbatar da zaman lafiya a Afrika ta tsakiya
2014-01-29 15:20:17 cri
A ranar 28 ga wata, kwamitin sulhu na M.D.D ya zartas da wani kuduri, inda ya tsawaita wa'adin ofishinsa wajen kokarin tabbatar da zaman lafiya a jamhuriyar Afrika ta tsakiya bisa tsawon shekara guda, wato har zuwa ranar 31 ga watan Janairu na shekarar 2015.

Kudurin ya bukaci da a kara inganta ayyukan ofishin da suka hada da taimaka wa yunkurin kafa gwamnatin wucin gadi ta kasar, taimakawa kawo karshen zubar da jina, samar da agajin jin kai ga kasar, da kuma taimakawa sabbin hukumomin wajen tafiyar da harkokin kasa domin bada hidima mai kyau ga jama'a, tare da tabbatar da tsaro da kare hakkin dan Adam a wannan kasa dake tsakiyar Afrika.

Kudurin ya dora muhimmanci sosai game da halin tsaro dake ci gaba da tsananta, da rashin doka, inda aka dora muhimmanci sosai kan mummunan tasirin da rikicin jamhuriyar Afrika ta tsakiya ke kawo wa shiyyar tsakiyar Afrika da sauran yankunan. Haka kuma, kudurin ya yi kira ga gwamnatin wucin gadi da ta sauke nauyin dake wuyanta, da kokarin samar da zaman lafiya da sulhuntawa tsakanin kabilun kasar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China