in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen dake gabashin nahiyar Afirka na hadin kai wajen fuskantar cutar Ebola
2014-08-10 16:41:30 cri
Wani jami'in ma'aikatar kiwon lafiya a kasar Kenya ya bayyana cewa, a halin da ake ciki kasashen dake gabashin nahiyar Afirka, na gudanar da hadin gwiwar daukar matakan dakile yaduwar cutar nan mai matukar hadari ta Ebola.

Jami'in wanda ya bayyana hakan jiya a birnin Nairobi, ya kara da cewa babban sakataren ma'aikatar kiwon lafiyar kasar Fred Segal, ya bayyanawa mahalarta wani taron tattaunawa game da hanyoyin hana yaduwar cutar ta Ebola cewa, a halin yanzu, kasashen dake gabashin nahiyar Afirka suna gudanar da hadin gwiwa a kan iyakokinsu, domin hana yaduwar cutar.

Haka zalika a cewarsa gwamnatocin kasashen sun karfafa matakan kandagarki, da na jan hankulan al'umma, tare da sayo kayayyakin binciken cutar da dai sauransu.

Bugu da kari, Mr. Segal ya kara da cewa, kasashen gabashin Afirka na mai da hankali sosai kan yanayin yaduwar cutar ta Ebola. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China