in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Sin zai je birnin Alkahira
2014-08-02 16:39:34 cri
Jiya Jumma'a 1 ga watan Agusta, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya bayyana cewa, ministan harkokin wajen kasar Wang Yi zai je birnin Alkahira, don yin shawarwari kan batun tsagaita bude wuta tsakanin Isra'ila da Falesdinu tare da wakilan Masar da kungiyar tarayyar kasashen Larabawa, da kuma yin hadin gwiwa wajen ciyar da aikin shimfida zaman lafiya a yankin gaba ta tsakiya.

Qing Gang ya ce, kwanan baya, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya sake jaddada matsayin kasar Sin kan batun yankin Gaza, inda ya yi kira da a kawo karshen musayar wuta ba tare da bata lokaci ba don kiyaye tsaron jama'ar yankin.

Minista Wang zai tafi birnin Alkahira don karfafa aikin shimfida zaman lafiya a yankin zirin Gaza. Rikicin da jama'ar yankin Gaza suke fama da shi a halin yanzu ya tayar da hankulan jama'ar kasar sosai, shi ya sa, kasar Sin ta riga kuma take ci gaba da ba da taimako yadda ya kamata ga Falesdinu da yankin Gaza. Bugu da kari, kasar Sin za ta ci gaba da yin hadin gwiwa tare da gamayyar kasa da kasa wajen cimma burin tsagaita bude wuta a yankin Gaza da kuma kiyaye zaman lafiyar yankin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China