in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya zuwa shekarar 2050 kashi biyu bisa uku na al'ummar duniya za su kaura zuwa birane
2014-07-11 16:06:21 cri
Wani sabon rahoton da MDD ta fitar a ran 10 ga wata, ya nuna cewa, a halin yanzu, rabin mutanen duniya na zaune ne a birane, kuma ya zuwa shekarar 2050, kashi biyu bisa uku na al'ummar duniya za su kaura zuwa birane.

Ofishin kula da yawan al'umma na hukumar kula da harkokin tattalin arziki da zaman takewar al'umma ta MDD ne ya bayyana hakan, a yayin taron gabatar da rahoton game da binciken da aka yi kan makomar bunkasuwar biranen kasa da kasa na shekarar 2014 da aka yi a hedkwatarsa dake birnin New York a wannan rana.

Rahoton ya yi hasashen cewa, ya zuwa shekarar 2050, yawan al'ummar duniya zai karu da biliyan 2.5, kuma kashi tara bisa goma daga cikinsu za su kasance a biranen Asiya da Afirka, kana kasashen da za su samu karuwar yawan mutane mafi yawa a nan gaba su ne Indiya, Sin da kuma Najeriya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China