in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD da kungiyar AU sun tattauna kan ciyar da aikin tsaro da yaki da ta'addanci gaba cikin hadin gwiwa
2014-06-07 16:34:49 cri
Jiya Jumma'a 6 ga wata, kwamitin sulhu na MDD da kwamitin zaman lafiya na kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU sun yi taro a hedkwatar MDD dake birnin New York, inda suka tattauna kan hanyar ciyar da aikin kiyaye tsaro da yaki da ta'addanci a kasashen Afirka gaba cikin hadin gwiwa.

Shugaban kwamitin tsaron MDD a wannan karo, zaunannen wakilin kasar Rasha dake MDD Vitaly Churkin da shugaban kwamitin zaman lafiya na kungiyar AU na wanna karo, zaunannen wakilin kasar Uganda dake kungiyar AU Mull Sbujja Katende sun gana da kafofin watsa labarai cikin hadin gwiwa bayan taron.

Yayin da suka yi tsokaci kan 'yan matan da aka yi garkuwa da su a kasar Najeriya, Mr. Katende ya bayyana cewa, kasashen kungiyar AU na ci gaba da neman wadannan 'yan mata cikin sirri. Shugabannin kasashen kungiyar AU dukkansu sun samar da taimako ga gwamnatin kasar Najeriya, kuma wasu na ci gaba da ba da taimako ga gwamnatin kasar domin ceto wadannan 'yan mata cikin sauri.

Bugu da kari, Mr. Katende ya kara da cewa, kungiyar AU na mai da hankali sosai kan yin hadin gwiwa yadda ya kamata da MDD wajen yaki da ta'addanci, kuma tana son ci gaba da karfafa musayar labaran yaki da ta'addanci dake tsakanin bangarorin biyu a nan gaba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China