in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Biranen gabashin Afrika biyu suke kan gaba ta fuskar samun cigaba in ji AT Kearney
2014-04-18 10:15:44 cri
Cibiyar kula da cigaban birane ta AT Kearney ta fitar da wani sabon binciken data gudanar game da yanayin bunkasuwar birane na shekarar 2014 a duniya, inda ta yi hasashen cewa, biranen Addis Ababa da Nairobi dake Afrika ta gabas suna cikin birane goma a duniya da suka fi samun kyakkyawar makoma ta fuskar samun cigaba.

Cibiyar ta zabi wasu birane daga cikin kasashe 34 da ba su samun kudin shiga mai yawa ba bisa ga alkaluman da bankin duniya ya tsara, domin gudanar da wannan bincike kan biranen dake cikin wadannan kasashe 34 bisa ganin ko za su iya daga matsayansu, ko a'a cikin shekaru 10 zuwa 20 masu zuwa. Birnin Addis Ababa na kasar Habasha ya kasance na uku, bayan biranen Djakarta na kasar Indonesia da kuma Manila na kasar Philippines, yayin da babban birnin kasar Kenya, Nairobi ya cike garbin na tara cikin jerin wadannan birane.

Kana wasu birane ukun nahiyar Afirka na daga cikin birane 20 dake kan gaba da wannan binciken ya shafa, su ne, biranen Johannesburg da Cape Down na kasar Afirka ta Kudu da kuma birnin Tunis na kasar Tunisia. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China