in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya zuwa shekarar 2020 adadin mutanen da za su zauna a birane zai kai kashi 60 bisa dari a kasar Sin
2013-07-08 16:34:13 cri
Kwanan baya, mataimakin shugaban cibiyar nazarin fasahar ci gaba a majalisar gudanarwar kasar Sin Han Jun, ya bayyana a Beijing, babban birnin kasar,cewa, ya zuwa shekarar 2020, adadin mutanen kasar Sin da za su zauna a birane zai kai kimanin kaso 60 bisa dari, yayin da adadin zai kai kashi 66 bisa dari a shekarar 2030.

Han Jun ya bayyana hakan ne yayin taron shekara-shekara na tattaunawa kan batun nazarin zaunannun kadarorin Sinawa na shekarar 2013.

Han Jun na ganin cewa, aikin raya garuruwa zai bunkasa tattalin arzikin kasar Sin, ta yadda zai iya kara bukatu, da kuma kudaden shiga ga jama'ar kasar. Amma, za a gamu da matsaloli da kalubale da dama yayin gudanar da aikin, kamar batun kwararar mutane zuwa birane daga kauyuka, wanda hakan ka iya haifar da mawuyacin hali gare su yayin zama tare da mutanen birane, kuma ba za su iya samun isasshiyar hidima ta kayan more rayuwa kamar yadda ya kamata ba, baya ga matsalar samun daidaito wajen bunkasa birane da dai sauransu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China