in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane fiye da dubu daya sun mutu a sakamakon hare-hare da rikice-rikicen da suka faru a kasar Iraki a wannan wata
2014-06-25 15:40:30 cri
Tawagar MDD mai bada taimako ga kasar Iraki ta gabatar da wani rahoto a ranar 24 ga wata, inda ta ce, mutane fiye da dubu daya sun mutu a sakamakon hare-haren dakarun ISIS da rikice-rikicen da suka faru a kasar Iraki a wannan wata.

A gun taron manema labaru da aka gudanar a cibiyar MDD dake birnin New York a wannan rana, kakakin babban sakataren MDD Stephane Dujarric ya bayyana cewa, bisa kididdigar da tawagar MDD mai bada taimako ga Iraki ta yi, an ce, yawan fararen hula da suka mutu a jihohin Ninevehdin, Diyala da kuma Salah ad Din ya kai 757, yayin da mutane 599 suka ji rauni. A birnin Baghdad da kuma yankin kudancin kasar, kuma mutane 318 ne suka mutu a sakamakon hare-hare, kana wasu mutane da dama sun rasu a sakamakon fashewar bom din da aka dasa a cikin mota.

Dujarric ya kara da cewa, babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya yi kira ga kasashen dake wannan yanki da su yi kokarin tabbatar tsaro da zaman lafiya a kasar Iraki da kuma ta Syria. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China