in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin kasar Iraki na ci gaba da musayar wuta da dakarun 'yan adawa
2014-06-18 15:29:15 cri
Rahotanni daga Iraqi na cewa sojojin kasar sun gwabza fada da dakarun 'yan adawa, a kokarin da suke yin a kwato yankunan gabashi, da na yammacin kasar daga dakarun.

An ce an harbe wasu fursunoni fiye da 10 dake tsare a wani kurkuku, yayin musayar wuta da aka yi tsakanin bangarorin biyu a jihar Diyala dake gabashin kasar.

A hannu guda kuma gwamnatin kasar ta Iraki ta dora alhakin abin da ke faruwa a kasar kan kasar Saudiyya, wadda ta zarga da samarwa 'yan adawar kudade da goyon baya.

Wata sanarwa daga ofishin firaministan kasar Irakin ta ce alhakin halin zubar da jini, da tashin hankalin dake wakana a kasar na wuyan kasar Saudiyya. Har ila yau sanarwar ta yi gargadi ga gwamnatin Saudiyyar da ta mai da hankali kan batutuwan da suka shafi cikin gidanta, da kuma daina nuna kyama ga mabiya akidar Shi'a dake kasarta. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China