in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai hare-hare ga birane biyu na kasar Iraki ta sama
2014-06-25 14:55:39 cri
Bangaren soja da 'yan sandan kasar Iraki sun bayyana cewa, an ci gaba da yin musayar wuta a wasu yankunan dake fama da rikici a kasar. Inda a ran 24 ga wata aka kai farmaki ga wasu birane biyu dake yammacin kasar ta sama. Ko da yake dai sojojin gwamnatin kasar sun kare kamfanin samar da mai mafi girma na kasar daga fadawa hannun 'yan adawa.

Wani dan sanda a jihar al-Anbar ya bayyana cewa, an kai hare-hare kan birnin Qaim da na Rutba dake jihar ta sama, hare-haren da suka haddasa mutuwar mutane a kalla 69. A halin yanzu, wadannan biranen biyu suna karkashin ikon dakarun ISIS masu adawa da gwamnati.

A gun taron manema labaru da aka gudanar a wannan rana, kakakin bangaren soja na kasar Iraki Qassim Atta ya musanta labarin dake cewa 'yan adawa suka kwace kamfanin samar da mai na Baiji, wanda shi ne mafi girma a kasar. Atta ya kara da cewa, yanzu haka jami'an tsaron kasar suna rike da ikon wannan kamfani. Kana sojojin gwamnatin kasar sun cimma nasarar fatattakar dakarun ISIS daga harabar kamfanin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China