Mr Atta ya bayyana hakan ne a gun wani taron manema labaru da aka yi a ranar 15 ga wata bisa agogon wurin, yana mai cewa cikin sa'o'i 24 da suka gabata, sojojin kasar Irakin sun harbe dakarun ISIS 279, tare da kwace birane da dama dake arewacin kasar daga ikon kungiyar.
Kaza lika Atta ya kara da cewa, sojojin kasar sun cimma nasarar dakile mamayar da yankunan kasar da dakarun ke kokarin yi. (Zainab)