in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kotun tarayya a Iraki ta amince da sakamakon zaben sabuwar majalisar dokokin kasar
2014-06-17 15:12:30 cri
Kotun tarayyar kasar Iraki ta bayyana amincewa da sakamakon zaben sabuwar majalissar dokokin kasar. Hakan dai na zuwa ne daidai lokacin da kasar ke fuskantar yanayin tabarbarewar tsaro, yayin da sojojin gwamnati da na dakarun 'yan adawa ke ci gaba da dauki ba dadi.

An dai gudanar da zaben sabuwar majalissar dokokin kasar ta Iraki ne a ranar 30 ga watan Afrilun da ya gabata, inda jam'iyyar "State of Law alliance" ta firaminista Nuri Al-maliki ta samu rinjaye, da kujeru 92 cikin daukacin kujerun wakilci 328.

A daya bangaren kuma babbar kwamishiyar MDD dake kula da harkokin kare hakkin bil Adama Navanethem Pillay ta bayar da wata sanarwa a birnin Geneva, inda ta ce ofishinta ya samu labari cewa, a 'yan kwanaki biyar da suka wuce dakarun kungiyar ISIL sun hallaka sojoji, da 'yan sanda, da sauran ma'aikatan gwamnatin kasar ta Iraqi da suka kame, da yawansu ya haura dari daya.

Pillay ta tabbatar da cewa, za a dauki wadannan ayyuka na kisan kai a matsayin laifukan yaki.

Kasar Iraqi dai ta auka hargitsi ne tun bayan janyewar da sojojin Amurka suka yi daga kasar a shekarar 2011 da ta gabata. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China