in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nahiyar Afirka ta amfana da ci gaban kasar Sin,inji AU
2014-05-02 16:26:21 cri
Mataimakin shugabar hukumar zartarwas kungiyar AU,Erastus Mwencha ya bayyana cewa, nahiyar Afirka tana amfana da bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin.

Jami'in na AU ya bayyana hakan ne ranar Alhamis, lokacin da ya ke zantawa da manema labarai na kasar Sin a Addis Ababa,babban birnin kasar Habasha,inda ya yaba da irin rawar da kasar Sin ke takawa ga ci gaban tattalin arzikin Afirka a cikin shekarun da suka gabata,musamman yadda kasar ta Sin ke bukatar kayayyakin nahiyar.

Mwencha ya ce,Sin da Afirka na tattaunawa don kara inganta dangantakar da ke tsakanin su a fannoni daban-baban ta hanyar dandalin nan na hadin gwiwar Sin da Afirka(FOCA). (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China