in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a gurfanar da kaftin din jirgin ruwan fasinjan da ya nutse a Koriya ta Kudu gaban kotu
2014-05-15 15:25:18 cri
Kamfanin dillancin labaru na Yonhap na kasar Koriya ta Kudu ya bayyana cewa, hukumar gabatar da kararraki ta kasar za ta gabatar da karar kisan kai, kan ma'aikata hudu na jirgin ruwan da ya nutse a kasar, ciki hadda kaftin din jirgin ruwan.

Wadannan ma'aikata za su fuskanci zargin da za a gabatarwa kotu da ya hada da laifin kisan kai, yunkurin kisan kai, da kuma gazawarsu wajen gudanar da aikinsu yadda ya kamata da dai sauransu.

Haka zalika, za a gabatar wa kotun alhakin rasa rai, ko jikkata sakamakon rashin kulawa, da kuma keta dokar aikin ceto a hadarin na teku ga sauran ma'aikata guda goma sha daya.

Jirgin ruwan fasinjan dai mai dauke da mutane 476 ya nutse ne a ruwan Koriya ta Kudu ranar 16 ga watan da ya gabata, inda aka samu nasarar ceto mutane 172 daga cikin fasinjojin, kuma ya zuwa yanzu akwai mutane 20 da ba kai ga sanin inda suke ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China