in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojan Koriya ta Kudu ta girke jiragen ruwan soja na Aegis guda biyu a tekun gabas da na yamma
2013-04-05 15:50:56 cri
Bisa labarin da aka samu daga kamfanin dillancin labarai na Yonhap ran 5 ga wata, an ce, rundunar sojan kasar Koriya ta Kudu ta girke jiragen ruwan soja na Aegis guda biyu a tekun gabas da na yamma don kakkabo makami mai linzami, wato idan Koriya ta Arewa ta harbo su.

Labarin ya kuma nuna cewa, rundunonin kasar Koriya ta Kudu da kasar Amurka suna ganin cewa, kila kasar Koriya ta Arewa ta yi gwajin harba makami mai linzami na matsakaicin zango wanda nisan tafiyarsa zai kai kilomita dubu 3 ko dubu 4, a wani filin gwajin da ke Musudan-ri na jihar Hamgyongbukdo,don haka za su kara karfin sa ido kan yunkurin da Koriya ta Arewa ke yi.

Bugu da kari, bisa labarin da kamfanin dillancin labarai na Yonhap ya bayar ran 4 ga wata, an ce, hukumomin leken asiri na Koriya ta Kudu da na Amurka sun samu labarin cewa, kasar Koriya ta Arewa ta riga ta yi jigilar makami mai linzami na matsakaicin zango, zuwa gabar tekun gabas. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China