in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara wani sabon zagaye na tattaunawa game da batun nukiliyar Iran a Geneva
2013-11-20 21:33:06 cri
Yau Laraba 20 ga wata agogon Geneva, kasar Iran da kasashen nan shida batun nukiliyar kasar Iran ya shafa suka fara wani sabon zagaye na tattaunawa game da batun nukiliyar kasar Iran a birnin Geneva na kasar Switzerland. Wakilai daga kasashen da abin ya shafa za su ci gaba yin tattaunawa don kulla wata yarjejeniya.

Yau Laraba 20 ga wata, an yi tattaunawa tsakanin kasashe biyu na kasashen da abin ya shafa, sai a ranar 21 ga wata, za a gudanar da cikakken zaman taro na kasashen nan shida batun nukiliyar kasar Iran ya shafa da kasar Iran.

Bisa labarin da aka samu, yau da yamma bisa agogon wuri, babbar wakiliyar EU mai kula da harkokin dipliomasiya da tsaro kungiyar EU Catherine Ashton za ta yi shawarwari tare da ministan harkokin waje, babban wakili mai kula da shawarwarin batun nukiliyar kasar ta Iran Mohammad Javad Zarif. Bugu da kari, tawagar kasar Sin dake karkashin jagorancin mataimakin ministan harkokin wajen kasar Li Baodong ta riga ta isa birnin Geneva, kuma yau da yamma, Mr. Li Baodong zai gana da wakilan kasashen Amurka da Rasha. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China