in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a hanzarta gudanar da shawarwari na sabon zaagaye kan batun nukiliyar kasar Iran
2013-09-06 15:47:44 cri
Ran 5 ga wata, a hedkwatar MDD da ke birnin New York, mataimakin zaunannen wakilin Sin da ke MDD Wang Min ya bayyana cewa, hanya daya tak kuma mafi dacewa wajen warware batun nukiliyar kasar Iran cikin zaman lafiya ita ce yin shawarwari. Shi ya sa ya kamata bangarorin da abin ya shafa su hanzarta gudanar da shawarwari na sabon zagaye kan batun nukiliyar kasar Iran da ke tsakaninta da kasashen shida da batun ya shafa da suka hada da kasashen Amurka, Burtaniya, Faransa, Rasha, Sin da kuma Jamus.

A wannan rana ne kuma, aka kira taron kwamitin sulhu na MDD, inda aka saurari rahoton da kwamitin yanke hukunci ga kasar Iran ya gabatar. Yayin taron, Wang Min ya ba da jawabi cewa, ya kamata bangarorin daban daban da abin ya shafa su dauki alhakin aiwatar da kudurin kwamitin sulhu na MDD yadda ya kamata, amma ainihin burin kudurin ba yin hukunci kan kasar Iran ba ne. A kullum kasar Sin na ganin cewa, ya kamata kwamitin yanke hukunci da kungiyar masana su ba da taimako wajen aiwatar da shawarwarin da ke tsakanin bangarorin da abin ya shafa bisa fahimta da kuma amincewar juna, ta yadda za a iya warware matsaloli ta hanyar diplomasiya. Kuma kamar yadda kasar Sin ta nuna a kullum cewa, ba ta amince da hanyoyin kawo wa kasar Iran barazana ko ci gaba da daukar sabon takunkumi kan kasar ba.

Wang Min ya kuma kara da cewa, kasar Sin na goyon bayan kasar Iran wajen karfafa hadin gwiwar dake tsakaninta da hukumar makamashin nukiliyar kasa da kasa, don samar da sakamako mai gamsarwa cikin sabon shawarwarin da za a yi ran 27 ga watan Satumba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China