in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Kwadibwa ta kara tura sojoji zuwa yammacin kasar don aikin zaman lafiya
2013-04-03 16:56:22 cri
Sojojin Jamhuriyar Kasar Kwadibwa, tawagar MDD da kuma sojojin kasar Faransan dake kasar, sun gudanar da taron shugabanni na hadin gwiwa a Abidjan babban birnin kasar a ranar 2 ga wata, inda suka tsai da kudurin kara tura sojojin Jamhuriyar guda 600 zuwa yankin yammacin kasar don aikin kiyaye zaman lafiya.

Hafsan hafsoshin sojojin Jamhuriyar Kasar Kwadibwa Soumaïla Bakayoko ya bayyana wa 'yan jarida cewa, sojoji guda 600 sun fara tashi zuwa yankin yammacin kasar tun daga ranar 1 ga wata, kuma mafi yawansu sun je jihar Toulepleu da sauran jihohi 2 dake makwabtaka da kasar Liberia.

Ya ce, wadannan sojoji za su fara aikin kiyaye zaman lafiya a kan iyakar kasar dake yankin yamma tun daga ranar 6 ga wata, don tabbatar da gudanar da zaben birane da garuruwa a yankin yadda ya kamata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China