in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kiran da a hanzarta shirya yadda 'yan gudun hijira za su kada kuri'unsu a zaben Mali
2013-07-24 10:40:09 cri
Kakakin MDD Martin Nesirky ya fada a ranar Talata cewa, yayin da aka shirya gudanar da zagayen farko na zaben shugaban kasar Mali a ranar Lahadi, hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD ta yi kira ga hukumomin kasar ta Mali, da su hanzarta shirya yadda 'yan kasar da ke gudun hijira za su kada kuri'unsu.

Nesirky ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai, inda ya ce, ofishin babbar kwamishinar kula da 'yan gudun hijira ta MDD(UNHCR) ya bayyana cewa, yana ci gaba da shiryawa tare da hukumomin kasar Mali da sauran kasashe makwabtaka, ta yadda wadanda ke gudun hijira za su kada kuri'unsu.

Kakakin na MDD ya ruwaito UNHCR din na cewa, yana da muhimmanci mahukuntan kasar ta Mali su hanzarta baje kolin rijistar masu zabe da raba katunan zabe a Burkina-Faso, Niger da Mauritania.

A cewar UNHCR, an yi kiyasin cewa, yawan 'yan gudun hijirar Mali da ke kasashen Burkina-Faso, Niger da kuma Mauritania sakamakon fadan Mali na baya-bayan nan ya kai 175,000.

Nesirky ya ce, rawar da hukumar za ta taka yayin zaben, ita ce taimakawa 'yan gudun hijira su yi zabe cikin yanayin tsaro. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China