in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya yi kira da a kwantar da hankali a Guinea sakamakon fadan kabilancin da ya barke a kasar.
2013-07-19 10:27:20 cri
A ranar Alhamis ne babban sakataren MDD Ban ki-Moon, ya bayyana matukar damuwa dangane da rahotannin da ake bayar wa na barkewar fadan kalibanci a kasar ta Guinea, inda ya yi kiran da a kwantar da hankali a kasar da ke yammacin Afirka.

A cikin wata sanarwa da kakakinsa ya rabawa manema labarai, Ban ki-Moon ya bayyana matukar rashin jin dadinsa, game da rahotannin barkewar fadan kabilanci a kudancin Guinea, lamarin da ya yi sanadiyar asarar rayuka da dukiyoyi da dama.

Sanarwar ta kuma yi kiran da a kwantar da hankali, kana babban sakataren ya bukaci 'yan kasar ta Guinea, da su guji aikata duk wani abin da zai kawo rashin zaman lafiya tsakanin al'ummomin da ke kasar.

Bugu da kari ya jaddada muhimmancin samar da yanayin da ya dace na zaman lafiya da gudanar da zabukan 'yan majalisun da aka shirya gudanarwa a ranar 24 ga watan Satumban wannan shekara.

A cewar rahotanni, adadin wadanda suka mutu a fadan da ya barke a daren ranar Lahadi a yankin N'Zerekore da ke kudancin Guinea ya karu zuwa 54 kana wadanda suka jikkata ya doshi 100. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China