in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Guinea ya amince da sabon lokacin da za gudanar da zaben 'yan majalisar dokoki
2013-07-11 11:00:33 cri
Ran 10 ga wata, shugaban kasar Guinea Alpha Conde ya amince da jadawalin zaben 'yan majalisar dokokin kasa da kwamitin zabe mai zaman kansa ya mika masa, inda ya sanar da gudanar da zaben 'yan majalisar dokokin kasar a ranar 24 ga watan Satumba, bayan jinkirtar da shi har sama da shekaru biyu.

Bugu da kari, shugaba Conde ya bukaci kwamitin zaben da dai sauran hukumomin da abin ya shafa da su dukufa wajen shirya ayyukan zabe.

A sa'i daya kuma, ya yi kira ga jam'iyyun daban daban da su shiga zaben cikin lumana don a tabbatar da yanayin tsaron zaben.

Ran 8 ga wata, kwamitin zabe mai zaman kansa na kasar Guinea ya kira taron dukkan mambobinsa, inda suka tsai da jadawalin zaben 'yan majalisar dokokin kasar, kuma an tsara wannan jadawali ne bisa yarjejeniyar da aka kulla a farkon watan da muke ciki, tsakanin jam'iyyar dake kan gadon mulki da jam'iyyar adawa, kan batun zaben 'yan majalisar dokoki, kuma ya kamata a gudanar da zaben bayan kwanaki 84 da kulla wannan yarjejeniya. Bisa tsarin mulkin kasar da aka tsayar an ce,

duk kudurorin da kwamitin zabe mai zaman kansa ya tsayar ba za su fara aiki ba sai bayan shugaban kasa ya amince da su. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China