in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 54 sun rasu sanadiyyar barkewar rikici tsakanin wasu kabilu biyu a kasar Guinea.
2013-07-18 16:33:02 cri
Ran 17 ga wata, bisa labarin da sashen kiwon lafiya ta kasar Guinea ta fitar, an ce, ya zuwa yanzu, mutane 54 ne suka rasu a sanadiyyar rikicin da ya barke tsakanin wasu kabilu biyu ranar 15 ga wata, a yankin Nzerekore, Baya ga wasu darurruwa da suka ji raunuka.

Amma, har zuwa yanzu, gwamnatin kasar ta Guinea ba ta fitar da sabon jerin sunayen wadanda suka rasa rayukan nasu yayin ricikin ba. Sai dai rahotanni na baya sun bayyana cewa mutane 16 ne aka tabbatar sun rasa rayukansu, inda kuma wasu 80 suka jikkata. Wannan dai yanki na Nzerekore na da nisan kilomita dubu 1 ne da babban birnin kasar ta Guinea, yana kuma yankin kudu maso gabashin kasar.

An dai ce ranar 15 ga wata, wani dan sanda dan kabilar Guerze ya harbe wani direba dan kabilar Konianke, yayin da ake tsaka da takaddama kan zargin sace wani abu, matakin da ya harzuka 'yan kabilar wanda aka harbe, inda nan take suka fara daukar fansa, wanda hakan ne ya haddasa barkewar rikicin da ya janyo asarar rayuka da dama tsakanin 'ya'yan kabilun biyu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China