in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rattaba hannu kan yarjejeyinar kawo karshen rikici a kasar Guinea-Bissau
2012-05-21 11:24:53 cri
A ranar Lahadi majalisar dokokin kasar Guinea-Bissau, jam 'iyyun siyasa guda 25 na bangaren adawa na kasar, da kuma shugabannin sojin da suka gudanar da juyin mulki a ranar 12 ga watan Afrilu , sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta neman fito da kasar daga cikin rikici, inda aka amince da kafa wata sabuwar hukumar zabe mai zaman kanta.

Cewar shugaban majalisar dokokin kasar , Ibrahima Sory Diallo, ya sa hannu kan wannan yarjejeniya, kamar yadda shugabannin sojin da suka yi juyin mulki suka sa hannu wanda hafsan hafsoshin kasar Antonio Injai ya sama hannu a madadin su, da kuma jam'iyyun siyasa guda 25, wadanda suka hada jam'iyyar PRS ta Kumba Yala, wadda kafin juyin mulkin ta kasance babbar jam'iyyar adawa ta kasar. Jam'iyyar PAIGC ta tsohon firaminista Carlos Gomes Junior ba ta sa hannu ba kan wannan yarjejeniya.(Abdou Halilou).

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China