in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar Tarayyar kasashen Afrika AU ta bukaci amincewar gama kai a game da matsalar kasar Afrika ta tsakiya
2013-03-28 20:20:54 cri
Kungiyar Tarayyar kasashen Afrika AU ta bukaci gama kai wuri daya domin tinkarar matsalar kasar Afrika ta tsakiya wanda kungiyar 'yan adawa ta SELEKA ta karbe mulkin ta da karfin tuwo duk da yarjejeniyar da aka cimma a taron sulhun da akayi a watan Janairu.

Kwamnishinan zaman lafiya da tsaro na kungiyar AU Ramtane Lamamra,shi ne ya bayyana wannan bukatar a lokacin da ake taron kungiyar tarayyar kasashen BRICS a kasar Afrikan ta kudu..

A ganawar sa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua ya ce akwai bukatar haduwa gu daya a tsaida maganar yadda za'a shawo kan wannan matsala ta kasar Afrika ta tsakiya sannan kuma har ila yau akwai bukatar a mara ma kasar baya domin ta maido da doka da oda. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China