in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jama'a sun fara tafiyar da harkokinsu kamar yadda suka saba a gundumar Lushan ta kasar Sin inda aka samu bala'in girgizar kasa
2013-04-26 15:05:34 cri

Yau Jumma'a 26 ga wata ya zama mako daya da aka fara gudanar da aikin ceto a lardin Sichuan, inda girgizar kasa mai karfin digiri 7 bisa na'aunin Richer ya abku, ana kokarin ceton mutane da suke raye, kuma abin da ya fi nuna muhimmanci shi ne ba da agaji da yin rigakafin yaduwar wasu cututuka. Ban da haka kuma, matsalolin da suke adabar jama'a a fannin zaman rayuwarsu suna ta samun daidaituwa, jama'a sun fara tafiyar da harkokinsu kamar yadda suka saba a wuraren da suka gamu da bala'in.

Mataimakin shugaban lardin Sichuan Zhong Mian ya bayyana a gun taron manema labaru da aka yi a ranar Alhamis 25 ga wata cewa, har ila yau aikin ceto da ba da jiyya ga wadanda bala'in ya galabaitar da su, wani muhimmin aiki ne cikin wani lokaci a nan gaba. Ba shakka za a dudduba sosai a duk wuraren da gine-gine suka ruguje domin ceto mutane.

Ya zuwa yanzu, ba'a samu yaduwar cututtuka a wurin ba, kuma ana daidaita batun kiwon lafiya yadda ya kamata. Sannan an yi kokarin samar da ruwan sha mai tsabta ga mazaunan wurin.

Firaministan kasar Kazakhstan Serik Akhmetov, da firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu da dai sauran shugabannin kasa da kasa sun buga wayar tarho ko aiko da wasiku ga shugabannin kasar Sin domin nuna juyayi da boyon baya ga gwamnati da jama'ar kasar Sin game da wannan batu.

Ya zuwa karfe 6 da maraice na ran 24 ga wata, yawan mutane da suka rasa rayukansu sabo da bala'in ya kai 196, sannan 21 sun bace, kuma wasu 13,484 sun samu rauni. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China