in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Li Keqiang ya shirya ayyukan bada ceto a garin Lushan
2013-04-24 20:45:49 cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya gudanar da taron majalisar gudanarwar kasar Sin a ranar 24 ga wata a nan birnin Beijing, inda ya shirya ayyukan bada ceto a garin Lushan dake fama da bala'in girgizar kasa.

Li Keqiang ya bayyana a gun taron cewa, ya kamata a ci gaba da bada ceto ga mutanen da suka gamu da bala'in, da tsugunar da jama'ar dake fama da bala'in, bada kudin taimako ga jama'a, tabbatar da samar da gidajen kwana, abinci, ruwa ga mutane dake yankin, kara sa lura kan aikin kiwon lafiya, dawo da harkokin rayuwar jama'a a yankin da kuma kaddamar da aikin sake gina yankin cikin lokaci. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China