in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Sin ta nuna godiya ga kasa da kasa da suka nuna goyon baya ga kasar Sin wajen bada ceto da sake ginawa bayan abkuwar girgizar kasa a garin Lushan
2013-04-23 20:30:54 cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya bayyana godiyar gwamnatin kasar Sin ga kasashen duniya bisa ga jajantawar da suka nuna mata, da kuma nuna goyon baya ga Sin cewa za su bada taimakonsu domin sake gina wurin da girgizar kasar ya abku.

Firaminista Li ta bayyana hakan ne a yau Talata 23 ga wata a birnin Beijing, fadar gwamnatin kasar.

Bisa kididdigar da hukumar kula da harkokin jama'ar lardin Sichuan ta yi, an ce, ya zuwa karfe 6 na safiyar ranar 23 ga wata, mutane 193 sun rasa rayukansu a sakamakon girgizar kasa mai karfi maki 7 da ta abku a garin Lushan dake lardin Sichuan, mutane 25 sun bace, sannan kuma mutane 12211 sun ji rauni. Kana mutane fiye da miliyan 1.99 suna fama da bala'in.

Haka kuma, bisa kididdigar da ofishin bada umurni na hukumar 'yan kwana-kwana ya yi, an ce, ya zuwa karfe 8 na safiyar ranar 23 ga wata, an ceci mutane 165 da suka gamu da bala'in, guda 150 a cikinsu sun tsira da ransu. Kana an kaura jama'a 6976 zuwa wurin daban. A halin yanzu, ana ci gaba da yin aikin bada ceto a yankin dake fama da bala'in. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China