A yau Alhamis 18 ga wata, MDD ta fitar da wani rahoton dake cewa, an samu koma bayan tattalin arziki a shekara da muke ciki a yankin Asiya-Pacific, amma bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin ta hanyar irin nata za ta kawo tasiri sosai ga wannan yanki.
Rahoton ya ce, shirin shekaru biyar-biyar karo na 12 na raya kasar Sin da Sin ta dauka ya ba da tabbacin gaggauta canja hanyar raya tattalin arzikin kasar, don haka, Sin na kokarin a shirinta na kawar da talauci, ba da tabbaci ga manoma wadanda suke aiki a birane.
Wannan kwaskwarima da Sin take yi inji rahoton ya sa kasar ta samu ci gaban tattalin arziki ba tare da yin la'akari da wasu bambance-bambance ba, kuma hakan zai kawo tasiri mai amfani ga sauran kasashe dake yankin Asiya-Pacific.(Amina)