in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ziyarar shugaban kasar Jamus mr. Joachim Gauck a kasar Sin
2016-03-14 09:30:16 cri

Ziyarar da shugaban kasar Jamus mr. Joachim Gauck zai fara a kasar Sin a ranar 20 zuwa 24 ga watan March, 2016 yana jan hankalina sosai bisa la'akari da tasirin kasashen 2 ta fannin tattalin arzikin duniya da kuma tasirin da kasashen Sin da Jamus suke da shi ta fannin samar da zaman lafiya a dud duniya. Kana kasashen Sin da taraiyar kasar Jamus sun kafa huldar diplomasiya da cinikaiya da musayar al'adu a tsakaninsu a shekarar 1972. Muna fata wannan ziyarar da shugaban Jamhuriyar kasar Jamus mr. Joachim Gauck zai yi a jamhuriyar Jama'ar Sin bisa gaiyatar da shugaban kasar Sin shehun malami Xi Jinping ya yi ma shugaban kasar Jamus za ta kara inganta abokantaka da kuma huldar jakadanci a tsakaninsu zuwa wani saban mataki mai kyau.

Daga Alhaji Ali kiraji Gashua.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China