logo

HAUSA

CMG Ta Fitar Da Manyan Labarai 10 Da Suka Faru A Kasar Sin Da Wasu 10 Da Suka Faru A Kasashen Ketare A Shekarar 2020

2020-12-29 15:13:53 CRI

Manyan labarai 10 na cikin gidan kasar Sin

  1. Kasar Sin ta samu manyan sakamako wajen yaki da cutar COVID-19 a duk fadin kasar
  2. Zama na 5 na kwamitin tsakiya na Jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 19 ya tsara shirin raya kasa na shekaru 5 karo na 14 da kuma katafaren burin da ake son cimmawa zuwa shekarar 2035
  3. An kammala ayyukan kawar da talauci a daidai lokacin da aka tsara a kasar Sin
  4. Yayin da take fuskantar kalubale, kasar Sin ta zama kasa daya tilo da ta samu ci gaban tattalin arziki a duniya
  5. Cika shekaru 40 da kafa yankin musamman na tattalin arziki na Shenzhen da cika shekaru 30 da rayawa da bude kofar yankin Pudong, alamu ne na kasar Sin wajen kai wani babban mataki a fannin bude kofarta ga kasashen ketare
  6. Kasar Sin ta zartar da kundin dokar da ta shafi kyautata zaman rayuwar al’umma
  7. An samu ambaliyar ruwa mai tsanani a larduna 28 dake fadin kasar Sin, sannan an samu gagagrumar nasara a ayyukan tunkarar ambaliyar da na jin kai
  8. Kasar Sin ta yi bikin cika shekaru 70 bayan dakarun sa kai na kasar sun turjewa mamayar Amurka tare da taimakawa kasar Korea ta Arewa.
  9. Kasar Sin na ta samun nasarori akai-akai a fannin kimiyya da fasaha, kuma sakamakon da take samu a fannin kirkire-kirkire na karfafa gwiwa tare da jan hankali duniya
  10. Zaunannen kwamitin majalisar wakilan al’ummar kasar Sin ya zartar da dokar tsaron kasa kan yankin musammam na Hong Kong

Manyan labarai 10 na ketare

  1. Barkewar cutar COVID-19: Girmama kimiyya da hadin kai domin yaki da annobar ta zama matsayar da duniya ta cimma
  2. Cikar shekaru shekaru 75 da kafuwar MDD: kasashen duniya sun yi kira da karfafa hadin gwiwa da dangantakar kasa da kasa
  3. Yayin da tattalin arzikin duniya ke cikin mawuyacin hali, kasar Sin ta zama kasa daya tilo da ta samu ci gaban tattalin arziki a duniya  
  4. Kasashen yankin Asiya da Fasifik 15 sun rattaba hannu kan hadin gwiwar kafa yankin ciniki cikin ‘yanci domin kara kwarin gwiwa kan tattalin arzikin duniya
  5. Rashin tabbas kan tsarin sake gina yankin Gabas ta Tsakiya na karuwa, biyo bayan matsin lamba mai tsanani da Amurka ke wa Iran
  6. Shekaru 5 da rattaba hannu kan yarjejeniyar Paris: kasar Sin na tunkarar matsalar sauyin yanayi yadda ya kamata, tare da sauke nauyin dake wuyanta a matsayinta na babbar kasa
  7. Fara aiki da yankin ciniki cikin ‘yanci na nahiyar Afrika zai bude sabon babi ga ci gaban hadin gwiwar kasashen nahiyar
  8. Wariyar launin fata, rashin amincewa da juna tsakanin jam’iyyun Amurka biyu da bambancin dake tsakanin masu arziki da matalauta sun haifar da rabuwar kan al’ummar kasar
  9. Kasashe da dama sun shiga aikin binciken duniyar Wata da duniyar Mars
  10. Rikici ya barke tsakanin kasashen Azerbaijan da Armenia    

Fa’iza Mustapha