in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Danyen man da Sudan ta Kudu take hakowa a rana ya karu da ganga dubu 5
2019-05-02 16:19:45 cri
Jiya Laraba 1 ga watan Mayu, ma'aikatar harkokin man fetur ta kasar Sudan ta Kudu ta sanar da cewa, tun daga jiyan ne aka dawo da aikin hakar danyen mai a filin hakar man na El-Nar, inda a baya aka dakatar da aikin hakar man fetur sakamakon yakin basasa a kasar. Yanzu ana hakar danyen man fetur ganga dubu 5 a ko wace rana. Kana Sudan ta Kudu tana hakar man da ya kai ganga dubu 175 a ko wace rana baki daya.

Ministan man fetur na kasar Sudan ta Kudu Ezekiel Lol Gatkuoth ya bayyana wa wakilin kamfanin dillancin labaru na Xinhua cewa, kasarsa ta gode wa kokarin da kamfanin man fetur da iskar gas na kasar Sin wato CNPC ya yi wajen sake dawo da aikin hakar danyen mai a filayen hakar man fetur na kasar, lamarin da zai taimakawa kasarta Sudan ta Kudu ta kama hanyar farfado da tattalin arzikinta cikin sauri. Ministan ya kuma nuna cewa, sakamakon dawo da aikin hakar man fetur a filayen hakar man El Toor da Manga da za a yi a karshen watan Mayun bana daya bayan daya, ya sa ana sa ran ganin yawan danyen man fetur da kasar Sudan ta Kudu take hakowa a kowace rana zai karu da ganga dubu 70 baki daya. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China