in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon kasar Sin ya bukaci goyon bayan kasa da kasa wajen warware batun siyasar Syria
2019-03-28 09:01:28 cri

Mataimakin wakilin din-din-din na kasar Sin a MDD Wu Haitao, ya yi kira ga al'ummomin kasashen duniya, da su ci gaba da sa kaimi wajen ganin an warware batun Syria ta hanyar siyasa.

Wu Haitao wanda ya bayyana haka a taron kwamitin sulhu, ya ce, shekarun da aka kwashe ana tashin hankali a kasar ta Syria, ya haifar wa kasar da ma al'ummar ta mummunan kunci. Don haka al'ummar Syria na bukatar samun zaman lafiya cikin hanzari ta yadda za su koma, su kuma farfado da rayuwarsu kamar yadda aka saba.

Ya ce, ya kamata MDD ta zurfafa tsare-tsaren da take yi da gwamnatin Syria, ta yadda za a hanzarta kafa kwamitin da zai shata kundin tsarin kasar wadda zai kunshi kowa ya kuma samu amincewar dukkan bangarori.

Jami'in na kasar Sin ya kuma bayyana cewa, wajibi ne a yi la'akari da bukatun bangarorin da abin da ya shafa yadda ya kamata, ciki har da gwamnatin Syria, ta yadda za a kafa tsarin siyasa mai nagarta da zai dore.

Ya bukaci al'ummomin kasa da kasa, da su karfafa hadin gwiwar yaki da ayyukan ta'addanci a kasar Syria, da amfani da ingantaccen tsari don yakar dukkan kungiyoyin 'yan ta'adda da kwamitin sulhu ya zayyana, don ganin ba su sake dawowa ba.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China