in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakada: Sin za ta cigaba da yin hadin gwiwa da Syria a bangaren yada labarai
2018-07-05 11:05:48 cri

Jakadan kasar Sin a Syria Qi Qianjin, ya bayyana muhimmancin cigaba da hadin gwiwa tsakanin Sin da Syrian a bangaren watsa labarai.

Da yake jawabi a hedkwatar jaridar al-Watan ta kasar a Damascus, Qi ya yaba da irin hadin gwiwar dake wanzuwa tsakanin kasashen biyu a cikin shekaru 7 da suka gabata a matakai daban daban, ciki har da hadin gwiwar kasashen a bangaren yada labaru.

Jakadan ya ce, "muna sha'awar wannan hadin gwiwa, kuma muna son mu ci gaba da hadin gwiwar a wannan bangare. Muna yin tunani game da sabbin ayyukan yin musaya tsakanin 'yan jaridun Sin da na Syria a nan gaba".

A nasa bangaren, Waddah Abd Rabbo, babban editan jaridar ta al-Watan ya ce, kafafen yada labaran Syrian suna bukatar a ci gaba da taimaka musu sakamakon kalubalolin da suke fuskanta a sanadiyyar tashin hankalin da kasar take fama da shi.

"Muna son cigaba da yin hadin gwiwa da Sin" in ji Abd Rabbo.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China