Wakilin musammam na kasar Sin game da rikicin kasar Syria, Xie Xiaoyan, ya ce kasar Sin za ta ci gaba da tuntubar bangarorin dake da alaka da rikicin Syria da aiki don ganin an hau teburin sulhu tare kuma da ba da gudummuwa wajen ganin an warware rikicin a siyasance.
Xie Xiaoyan wanda ke ziyara a Moscow, ya bayyana haka ne a jiya, inda ya ce kasar Sin za ta ci gaba da samar da agaji ga 'yan gudun hijirar Syria dake ciki da wajen Syria.
Yayin ziyarar, jami'in ya gana da mataimakin Ministan harkokin wajen Rasha Mikhail Bogdanov, inda suka tattauna game da matsalolin Gabas ta Tsakiya. (Fa'iza Mustapha)