Yau Laraba ne, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan birnin Beijing cewa, kasar Sin na son hada kai tare da kasar Rasha da ma sassan masu ruwa da tsaki daban-daban don ciyar da aikin warware batun Sham a siyasance gaba.
Kwanan baya ne, shugaba Vladimir Putin na Rasha ya sanar da fara janye sojojin kasar daga Sham. (Tasallah Yuan)