in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masanin Iran: kasar Sin na tinkarar matsaloli da batutuwa ba tare da rufa-rufa ba
2019-03-06 13:45:13 cri
Jiya Talata ne aka bude taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin NPC a nan Beijing, inda firaministan kasar Li Keqiang ya karanta rahoton ayyukan gwamnatin.

Mohsen Shariatinia, wani masani harkokin kasar Sin a jami'ar Shahid Beheshiti ta kasar Iran ya bayyana jiya cewa, abin da ya fi burge shi a rahoton ayyukan gwamnatin Sin, shi ne yadda kasar take tinkarar matsaloli da batutuwan masu alaka da tattalin arziki da zaman al'ummar kasar ba tare da rufa-rufa ba, inda kuma ta yi alkawarin ci gaba da warware su ta hanyar raya tattalin arzikin kasar.

Rahoton ya ce, karuwar GDP ta kasar Sin ta kai kaso 6.6 bisa dari a shekarar 2018, yayin da ta tsara wani shiri game da karuwar GDP a shekarar 2019 wato zai kai kaso 6 bisa dari zuwa kaso 6.5 bisa dari.

Yayin da Mohsen Shariatinia yake zantawa da 'yan jarida game da batun na tattalin arziki, ya ce, a shekarun baya, karuwar tattalin arzikin kasar Sin ta ragu sannu da hankali, saboda Sin ta shiga sabon tsarin yau da kullum kan tattalin arziki. Hakan ya nuna cewa, kasar Sin tana neman kara darajar kayayyaki ta hanyar nazarin kimiyya, a maimakon gurbata muhalli, da bata makamashi da yawa, da dogaro da sayar da kayayyaki zuwa ketare. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China