Majalisar kula da kundin tsarin mulkin kasar Senegal, ta sanar da sakamakon zaben shugaban kasar a hukumance, inda ta ayyana Mack Sall a matsayin wanda aka sake zaba, a zaben shugaban kasa da aka yi ranar 24 ga watan Fabrerun bana.
A cewar sakamakon da majalisar ta tantance, Macky Sall ya samu kuri'u 2,555,426 ko kuma kaso 58.26 na kuri'un da aka kada. Idrissa Seck ne kuma ya zo na biyu, da kuri'u 899,556 ko kuma kaso 20.51 na kuri'un. (Fa'iza Mustapha)