in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Senegal zasu karfafa dangantakarsu da kuma bunkasa hadin gwiwar Sin da Afrika
2019-01-07 17:02:06 cri
Kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasar Senegal domin bunkasa danganatakar dake tsakanin kasashen biyu da kuma kyautata hadin gwiwar Sin da Afrika zuwa matsayin dangantaka bisa manyan tsare tsare, in ji mamban majalisar gudanarwar kasar Sin kana ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi.

A lokacin ganawarsa da takwaransa na kasar Senegal Sidiki Kaba, Wang ya yabawa kasar Senegal saboda cigaba da goyon bayan da take baiwa kasar Sin game da batutuwan da suka shafi hakkokin kasar Sin game da muhimman muradunta, kana kasar Sin a shirye take ta nuna goyon bayanta ga kasar Senegal wajen samar da hanyar cigaban kasar da kiyaye moriyarta da hakkokinta.

Senegal tana sahun gaba cikin kasashen yammacin Afrika wajen sanya hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwar shawarar ziri daya da hanya daya (BRI), kuma a matsayinta na mai taimakawa jagorancin dandalin hadin kan Sin da Afrika (FOCAC), ta bude wani sabon shafi game dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, inji Wang.

A nasa bangaren, Kaba yace BRI, da sauran muhimman kudurori guda 8 dake shafar Afrika wanda shugaba Xi Jinping ya gabatar ya dace da ajandar kungiyar tarayyar Afrika na raya nahiyar nan da shekarar 2063 da manufar bunkasa Senegal wanda shugaban kasar Macky Sall ya gabatar, wanda zai haifar da babbar moriya da kuma samar da muhimmin sakamako na samun moriyar juna tsakanin Sin da Afrika.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China