in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IOC: Senegal za ta karbi bakuncin gasar Olympics ta 2022
2018-10-09 10:26:36 cri
Kwamitin shirya wasannin Olympic na IOC, ya tabbatar da Senegal, a matsayin kasar za ta karbi bakuncin gasar Olympic ajin matasa ta lokacin zafi, wadda za a yi a shekarar 2022.

Kwamitin na IOC ya yanke wannan shawara ne, a zaman sa na 133, wanda hakan ke nuna cewa, Senegal ce kasar Afirka ta farko da za ta karbi bakuncin gasar Olympic.

Kafin yanke wannan shawara, kasashen Botswana, da Najeriya, da Senegal da Tunisia, sun gabatar da bukatar su ta karbar bakuncin gasar. To sai dai kuma bayan duba na tsanaki, hukumar zartaswa, da jagororin IOCn, sun gamsu cewa Senegal ce mafi dacewa da gasar.

Da yake tabbatar da hakan, shugaban IOC Thomas Bach, ya ce kasashen Afirka sun goyi bayan Senegal, bisa bukatarta, ta karbar bakuncin wannan gasa dake tafe a shekarar 2022. Ya ce Senegal na da tarin matasa, da kuma sha'awar wasanni, don haka wannan dama ce ga Afirka, kuma dama ce ga kasar Senegal.

Biranen kasar uku da suka hada da fadar mulkin ta wato Dakar, da sabon birnin Diamniadio, da kuma birnin Saly na bakin ruwa ne za a yi amfani da su, wajen gudanar da wannan gasa. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China