in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara jefa kuri'a a zaben shugaban kasa a Senegal
2019-02-24 20:23:06 cri
Tun da misalin karfe 8:00 na safiyar yau Lahadi ne al'ummar kasar Senegal suka fita rumfunan zabe don zabar shugaban kasar, mutane sama da miliyan 6 ne suka yi rejista inda ake sa ran za su jefa kuri'unsu a duk fadin kasar har ma da ketare

Daga cikin 'yan takarar da za su fafatawa a zaben har da shugaban kasar mai ci Macky Sall, da tsohon firaiministan kasar Idrissa Seck, da tsohon ministan harkokin wajen kasar Madicke Niang, da wani malamin jami'a Issa Fall, da kuma tsohon jami'in hukumar tattara hajarin kasar Ousmane Sonko. Ana ganin fafatawar za ta fi zafi ne tsakanin Seck da shugaba mai ci Macky Sall. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China