Barkewar cutar huhu mai yaduwa ta yi sanadin mutuwar shanu 368 a jihar Kaduna dake arewacin Nijeriya.
A cewar gwamnatin jihar Kaduna, cutar wadda ta yadu zuwa sassan jihar, ta kama wasu shanu 764.
Kakakin fadar gwamnatin jihar Dahiru Abdullahi, ya ce shanu 764 da suka kamu da cutar na cikin mawuyacin hali.
Cutar huhun, cuta ce da ake samu daga kwayoyin cuta na bacteria, wadda ke yaduwa tsakanin shanu da dangoginsu. (Fa'iza Mustapha)